24 Janairu 2026Sojoji sun sha alwashin kuɓutar da masu ibada da aka sace a Kaduna

Date:

 

NNPP ta mayar wa Abba Kabir martani kan ficewa daga jam’iyyar

...

facebook/Abba Kabir Yusuf

Jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) ta yi kakkausar suka kan matakin da gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya ɗauka na ficewa daga jam’iyyar, inda ta bayyana matakin a matsayin rashin mutunta masu kaɗa ƙuri’ar da suka ba shi gagarumin goyon baya a zaɓen gwamna na 2023.

A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran jam’iyyar na ƙasa, Ladipo Johnson ya fitar, jam’iyyar ta ce matakin da Gwamna Yusuf ya ɗauka tamkar cin amanar al’ummar jihar Kano ne, wanɗanda a cewarta, sun kaɗa masa ƙuri’a ne sakamakon daɗewar da ya yi yana tare da tafiyar siyasar Kwankwasiyya.

”Muna matuƙar takaicin yadda Gwamna Abba, mutumin da al’ummar Jihar Kano suka damka wa al’ummar Jihar kan karfin biyayya da sadaukarwar da ya yi na tsawon shekaru da dama da ya yi wa tafiyar Kwankwasiyya, a yanzu ya zaɓii ya ci amanar da aka miƙa masa.” in ji sanarwar

Ta kuma ƙara da cewa ”Wannan mataki na iya mayar da jihar hannun waɗanda suka daɗe suna adawa da ci gabanta da muradun al’ummarta.”

Jam’iyyar NNPP ta buƙaci magoya bayanta a Kano da su kwantar da hankalinsu tare da bin doka, su kuma yi taka-tsan-tsan kan duk wani abu da zai iya haifar da tarzoma a siyasance ko kuma ta da zaune tsaye.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Yield Hunters and Tax Dodgers Drive Naira Rates Spread Wider

Investors seeking to lock in high yields on Nigerian...

Naira breaks N1,400 barrier at N1,396.99/$

Nigeria’s naira has traded below the N1,400/$1 level on...

NLNG unveils new visual identities of the Nigeria Prizes

At a most inspiring press conference held in Lagos...

North Macedonia Hosts Interactive Educational Exhibition on Life of Holy Prophet

————————————–North Macedonia is hosting an interactive educational exhibition titled...